
Hukumar yaki da cin hanci da rashawa mai zaman kanta (ICPC) ta tabbatar da karbar takardar koke daga Alhaji Aliko Dangote ta hannun lauyansa a ranar Talata 16 ga Disamba 2025.
Takardar koken ta kunshi zargin Shugaban Hukumar NMDPRA Alhaji Farouk Ahmed, biyo bayan bidiyon hirar Dangote da jaridar RFI Hausa wanda ya karade shafukan sada zumunta a karshen makon daya gabata.
Hukumar ICPC a cikin sanarwar da ta wallafa ta hannun Jami’in Hulda da Jama’ar ta John Okor Odey ya ce hukumar ta ba da bayyana cewa za a binciki koken yadda ya kamata.




