Nijeriya

Yanzu-yanzu: APC ta lashe kananan hukumomi 20 na Ribas

APC ta lashe kananan hukumomi 20 cikin 23 na Ribas

Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta lashe kananan hukumomi 20 cikin 23 a zaben kansiloli da aka gudanar a ranar Asabar.

A daya bangaren kuma, jam’iyyar PDP wadda ita ce jam’iyya mai mulki kafin ayyana dokar ta-baci a watan Maris, ta lashe kananan hukumomi uku ne kacal a zaben.

Shugaban Hukumar Zaben Jihar Ribas (RSIEC) Dr. Michael Odey ne ya sanar da sakamakon a hedikwatar hukumar da ke Fatakwal a yammacin Lahadi.

Dr. Michael Odey ya kuma bayyana sunayen wadanda suka lashe zaben mataimakin shugaban kasa, sai dai kawo yanzu ba a bayyana sakamakon zaben kansilolin ba.

Jarida Radio

Barka da zuwa shafin Jarida Radio - Kafa Mai Inganci, domin samun labarai da dumi-dumi da zurfafa nazari da shirye-shiryen rediyo masu kayatarwa. Jarida Radio ba kawai dandalin labarai ba ne - murya ce ga al'umma.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Check Also
Close
Back to top button