Nijeriya

Gwamna Yusuf yayi barazanar kwace gidaje a Kwankwasiyya, Amana, Bandirawo

Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya bayar da umarnin zartarwa da ya umarci masu gidajen da ke rukunin Kwankwasiyya, Amana, da Bandirawo da su tare a gidajensu nan da watanni uku ko kuma su fuskanci kwacewa.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar a ranar Litinin

Umarnin ya biyo bayan rantsar da sabon kwamishinan raya gidaje a fadar gwamnatin Kano.

Ya kuma bukaci wadanda ba za su iya kaura ba da su yi la’akari da bayar da hayar gidajensu, yana mai jaddada kudirin gwamnati na ganin rukunin gidajen sun bunkasa.

Jarida Radio

Barka da zuwa shafin Jarida Radio - Kafa Mai Inganci, domin samun labarai da dumi-dumi da zurfafa nazari da shirye-shiryen rediyo masu kayatarwa. Jarida Radio ba kawai dandalin labarai ba ne - murya ce ga al'umma.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button