Nijeriya

Jihar Yobe: Gobara ta kona kasuwar Kariyari

Tare da lalata dakarori da kuma dukiyoyin al'umma

Daga Adamu Aliyu Ngulde

Rahotanni daga jihar Yobe a yankin Arewa maso Gabashin Najeriya na cewa gobara ta kona kasuwar Kariyari, da ke karamar hukumar Tarmuwa tare da lalata dakarori da kuma dukiyoyin al’umma.

Wata majiya ta shaidawa Jarida Radio cewa gobarar ta kona shaguna da rumfuna 1,600 sannan mata da dama sun tabka asara ya yin gobarar.

Hakazalika wani ganau ya ce “A yayin da nake magana da kai mahukunta sun kawo ďauki tare da zurfafa bincike domin gano musabbabin gobarar”.

A halin yanzu dai wadanda suka shaida faruwar lamarin sun bayyana irin girman asarar da aka yi, don hakane suke neman tallafin gwamnati da kuma kungiyoyi masu zaman kan su domin ganin sun kawo ďauki ga wadanda iftila’in ya rutsa da su.

Yayin tattaro bayanai game da gobarar, Jarida Radio ta lura da cewa hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Yobe wato (SEMA) ta na tattara bayanan wadanda suka yi asara domin tallafa musu.

Jarida Radio

Barka da zuwa shafin Jarida Radio - Kafa Mai Inganci, domin samun labarai da dumi-dumi da zurfafa nazari da shirye-shiryen rediyo masu kayatarwa. Jarida Radio ba kawai dandalin labarai ba ne - murya ce ga al'umma.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button