Afirka

Masar na asarar kudaden shiga na wata-wata kusan dala miliyan 800

Shugaban kasar Masar Abdel Fattah al-Sisi ya fada a ranar litinin cewa kasarsa ta yi asarar kudaden shiga na mashigar ruwa ta Suez wadda ta kai kusan dalar Amurka miliyan 800 saboda halin da ake ciki a yankin, yayin da ‘yan Houthi na kasar Yemen ke kai hare-hare kan jiragen ruwa a tekun Bahar Maliya.

Tun a watan Nuwamban shekarar 2023 ne mayakan Houthis suke kai hari kan jiragen ruwa a yankin tekun Bahar Rum, domin nuna goyon bayansu ga Falasdinawa a Gaza, kan yakin da Isra’ila ke yi, lamarin da ya kawo cikas ga harkokin sufurin jiragen ruwa a duniya, ta hanyar tilastawa jiragen ruwa gujewa mashigin Suez da ke kusa da su, da kuma durkutsar da harkokin kasuwanci a nahiyar Afirka, lamarin da ya kara tsadar sufuri.

Sanarwar da fadar shugaban Masar ta fitar ba ta yi nuni da Houthis kai tsaye ba, amma Sisi ya ce a watan Disambar bara ta janyo wa Masar asarar kusan dala biliyan 7 na kudaden shiga daga kogin Suez a shekarar 2024.

A baya-bayan nan ne kungiyar ta Yemen ta lashi takobin ci gaba da kai hare-hare kan jiragen ruwan Amurka a tekun Bahar Maliya, a matsayin martani ga munanan hare-haren da Amurka ta kai kan kasar Yemen, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane akalla 53 a ranar Asabar, a farmakin da sojojin Amurka suka kai a yankin gabas ta tsakiya mafi girma tun bayan da shugaba Donald Trump ya hau karagar mulki a watan Janairu.

Sun kuma ce a makon da ya gabata za su ci gaba da kai hare-hare kan jiragen ruwan Isra’ila da ke wucewa ta tekun Bahar Rum idan Isra’ila ba ta dage shingen da ta kakaba na shiga Gaza ba.

Jarida Radio

Barka da zuwa shafin Jarida Radio - Kafa Mai Inganci, domin samun labarai da dumi-dumi da zurfafa nazari da shirye-shiryen rediyo masu kayatarwa. Jarida Radio ba kawai dandalin labarai ba ne - murya ce ga al'umma.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button