Nijeriya

Gobara ta kona sansanin ýan gudun hijira a Borno

Gobara ta kona sansanin ýan gudun hijira

Daga Adamu Aliyu Ngulde

A wani labari mai firgici da kuma tada hankali na cewa gobara ta kona sansanin ‘Water Board’ da ke karamar hukumar Monguno a jihar Borno.

Lamarin ya faru ne a ranar 19 ga wannan wata na Afirilu, sannan an yi asarar gidajen tantuna akalla guda ďari.

Shaidun gani da ido sun shaida cewa gobarar ta fara ne daga karfe 10:40 na safiyar ranar Lahadi kafin daga bisani wutar ta karade dukkannin sassan sansanin.

Cikin abubuwan da aka yi asara a sansanin sun hada da; kayan abinci, makwanci da sauran kadarorin ýan gidin hijirar.

Har zuwa lokacin tattaro bayanai ba a gano musabbabin tashin gobarar ba. Hakazalika ana ci gaba da kiyasta girman asarar da aka yi sanadin gobarar.

Tuni dai jami’an bada agaji suka kai ďauki zuwa sansanin domin shawo kan gobarar da kuma kaucewa masu kwasar ganima, sannan jami’an kwana-kwana tare da mazauna sansanin sun yi nasarar kashe gobarar.

Har ila yau babu jikkata ko rasa rai a ya yin gobarar.

 

 

Jarida Radio

Barka da zuwa shafin Jarida Radio - Kafa Mai Inganci, domin samun labarai da dumi-dumi da zurfafa nazari da shirye-shiryen rediyo masu kayatarwa. Jarida Radio ba kawai dandalin labarai ba ne - murya ce ga al'umma.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button