Nijeriya

Gwamnatin Adamawa ta sanar da shirin jinya kyauta ga masu ciwon koda

Gwamnan Adamawa Fintiri ya sanar da shirin jinya kyauta ga masu ciwon koda

Daga Mubarak Aliyu

Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru a ranar Asabar ya sanar da shirin yin jinyar koda a kyauta a fadin jihar domin sauƙaƙawa ga marasa galihu da ke zuwa a Asibitin Kwararru da ke a nan birnin Yola.

Rahotonni sun bayyana cewa matsakaicin kudin jinyar koda ga mai fama da cutar a kowane mako zai iya kaiwa kimanin Naira dubu 100.

A baya, marasa lafiya da ke fama da cutar koda suna dogaro ne da Asibitin koyarwa na jami’ar Modibbo Adama da ke nan Yola, ko kuma su yi tafiya mai nisa don samun magani a makwabtan jihohi.

Jarida Radio

Barka da zuwa shafin Jarida Radio - Kafa Mai Inganci, domin samun labarai da dumi-dumi da zurfafa nazari da shirye-shiryen rediyo masu kayatarwa. Jarida Radio ba kawai dandalin labarai ba ne - murya ce ga al'umma.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button