Afirka

Shugabannin Congo da Rwanda sun gana a Qatar

Shugabannin kasashen biyu sun gana a Qatar, sun kuma yi kira da a tsagaita wuta a gabashin Kongo. Kasashen uku sun yi kira da a tsagaita bude wuta nan take a gabashin Kongo.

Shugaban Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango Felix Tshisekedi da shugaban Rwanda Paul Kagame sun yi shawarwari kai tsaye a karon farko tun bayan da ‘yan tawayen M23 da ke samun goyon bayan Rwanda suka kwace wasu manyan biranen kasar biyu a gabashin Congo.

A cikin wata sanarwar hadin gwiwa da suka fitar da Qatar, wadda sarkinta ya shiga tsakani a tattaunawar da aka yi a Doha, kasashen sun yi kira da a gaggauta tsagaita bude wuta a gabashin Kongo.

Jarida Radio

Barka da zuwa shafin Jarida Radio - Kafa Mai Inganci, domin samun labarai da dumi-dumi da zurfafa nazari da shirye-shiryen rediyo masu kayatarwa. Jarida Radio ba kawai dandalin labarai ba ne - murya ce ga al'umma.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button